1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ethiopian Airlines zai karbi Arik a Najeriya

Yusuf Bala Nayaya
August 30, 2017

Shugaban sashin da ke lura da harkokin kasa da kasa a kamfanin Ethiopian Airlines Esayas Woldemariam shi ya bayyana haka a zantawa da kamfanin dillancin labaran AP.

https://p.dw.com/p/2j746
Großbritannien Flugzeug von Arik Air landet in Heathrow
Hoto: Imago

Kamfanin jirgin sama da ke zama kan gaba wajen samun riba a Afirka ya bayyana cewa zai karbi harkokin gudanarwar kamfanin jiragen sama mafi girma a Afirka ta Yamma da ke da cibiya a Najeriya wato Arik Air. Shugaban sashin da ke lura da harkokin kasa da kasa a kamfanin Ethiopian Airlines Esayas Woldemariam shi ya bayyana haka a zantawa da kamfanin dillancin labaran AP, ya ce hakan na zuwa ne bayan da ma'aikatar harkokin sufurin jirgin sama a Najeriya ta gabatar da wannan bukata.

Gwamnatin Najeriya dai ta karbi harkokin gudanarwar kamfanin na Arik a farkon wannan shekara bayan tafka asarar da kamfanin ya yi, don haka a cewar Esayas a zantawarsa da kamfanin dillancin labaran na AP a shirye suke wajen samar da sauyi a kamfanin.

Kamfanin na Ethiopian Airlines ya kasance daya cikin manyan jirage a Afirka karbar harkokin kamfanin Arik kuma za ta sanya ya sake zama fitacce a Najeriyar da ke da karfin tattalin arziki.