Kasashen yankin yammacin Afirka za su fito a kudin bai daya
June 18, 2019Talla
An dai kwashe sama da shekaru 30 ana jiran ganin an samu kudin na bai daya a tsakanin kasashen. Shugaban kwamitin gudanarwa na kungiyar ta ECOWAS Jean Claude Brou ya ce a wannan jikon ba wani shamaki sai an yi kudin na bai daya na kasashen yankin yammacin Afirka duk da kalubalen da ya ce ke a gabansu.