1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola ta ɓulla kuma a wani yankin na Guinea

September 3, 2014

Gwamnatin Guinea ta ce ta gano wasu ƙarin mutane da suka kamu da cutar Ebola a wani yankin ƙasar da cutar ba ta kai ba tun can da farko.

https://p.dw.com/p/1D66p
Kind mit Ebola in Kailahun Sierra Leone 15.08.2014
Hoto: Carl De Souza/AFP/Getty Images

Wani babban jami'in kiwon lafiya da ke jagorancin kwamitin gaggawa da ke yaƙi da cutar ta Ebola a Guinea. Abubakar Sidiki Diakite ya ce an gano waɗanda ke ɗauke da ƙwayoyin cutar mutane guda tara a garin Damaro da ke cikin lardin Kerouane da ke a yankin kudu maso gabashi na ƙasar.

Ofishin ministan kiwon lafiya na ƙasar ya ce mutane 18 aka sakawa ido ana lura da su a yankin bayan da wani ɗan ƙasar Laberiya da ke fama da cutar ta Ebola ya shigo garin.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman