1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ebola na kama jarirai a Kwango

November 24, 2018

Wani kiyasi da hukumar lafiya ta duniya ta fitar, ya nunar da cewa ta samu rahoton cutar da ya tabbatar da cutar Ebola a jikin jarirai da kuma kananan yara 'yan kasa da shekaru biyu.

https://p.dw.com/p/38rXL
Kongo Beni - Gesundheitspresonal mit Schutzanzug bei Ebola Behandlungszentrum
Hoto: picture-alliance/AP Photo/A. K. Maliro

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce ta samu rahoton bullar cutar Ebola a wannan makon a Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango a tsakanin jarirai.

A cewar hukumar wannan mummunar alama ce ta yadda cutar ke kara yaduwa a Jamhuriyar Dimukuradiyyar ta Kwango wadda ke fama da rikici. 

Wani kiyasi na baya-bayan nan da hukumar ta WHO ta fitar, ya nunar da cewa sun samu rahoton cutar ta Ebola a jikin jarirai da kuma kananan yara 'yan kasa da shekaru biyu.

Haka nan ma ta samu rahoton kamuwa da cutar a tsakanin yara shida da shekarunsu suka kama daga biyu zuwa 17, yayin da aka samu wata mata mai dauke da juna biyu da ke dauke da cutar. 

Kwararru dai sun yi amannar cewa yaran na kamuwa da cutar ne ta hanyar shayar da su nonon uwa.

Matsalar na zuwa ne kwana guda bayan da hukumar ta lafiya ta duniya ta kaddamar da sabon yaki da cutar ta Ebola, a dai-dai lokacin da ake ci gaba da gwabza fada a tsakanin dakarun gwamnati da na 'yan tawaye a yankunan Kivu da Ituru da ke fama da bala'in Ebolan.