Dubban yan Afirka sun yi zanga-zanga a Tel Aviv
January 5, 2014Fiye da mutane 30.000 ne 'yan asalin kasashen Afirka suka gudanar da wata zanga-zangar lumana a wannan Lahadin a birnin Tel-Aviv na kasar Isra'ila. Masu zanga-zangar dai sun shiga kasar ta Isra'ila ne ta barauniyar hanya. Wannan dai shi ne wani babban taron gangami irin haka da aka gani cikin wannan kasa a cewar wata majiya ta yan sanda. Masu zanga-zangar na nuna rashin jin dadinsu ne ga halin hukumomin kasar na kin kula da duba halin da suke cikin a matsayinsu na wadanda suka yi gudun hijira, sannan da dakatar da wasunsu da hukumomin kasar suka yi, inda suke cewa mu duka 'yan gudun hijira ne, a bamu 'yancinmu, kuma a daina rufe mu a gidajan kaso, wadanda akasarin su sun daga tutar kasar Eritreya da ta Habasha.
Mawallafi: Salissou Boukari
Edita: Umaru Aliyu