Mutane na guje wa mahallansu a Nijar
April 9, 2019Talla
Kimanin fararen hula 88 ne rahotanni a watan Maris suka nunar da cewa an halaka su a yankin kudo maso gabashi na kasar da ke da yawan Sahara, adadin da ke da yawa idan aka kwatanta da jumullar wadanda aka halaka 107 a shekarar bara.
Babar Baloch da ke magana da yawun Hukumar kula da 'yan gudun hijirar ta MDD ya fada wa manema labarai a birnin Geneva cewa, abin takaici ne yawan adadin mutane da ke rasa rayukansu duk wata wadanda ba su ji ba ba su gani ba. Da dama dai mutanen da ke gujewa hare-haren na Boko Haram na fakewa a yankin Diffa.