1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban Musulman Myanmar ke tserewa tashin hankali

Usman Shehu Usman
September 1, 2017

Tashin hankali yasa 'yan kabilar Rohingya sun yi ta kwarara izuwa kasar Bangladesh inda yan kabilar ke gudun tsira da ransu bayan da jami'an tsaro ke kara tozartar da su

https://p.dw.com/p/2jEkV
Rohingya in Myanmar und Bangladesch
Hoto: picture-alliance/dpa/M.Alam

A cewar hukumomin kasar akalla mutane 400 suka mutu a jihar Rakhine, inda rikici ya barke bayan da masuadawa kuncin rayuwar da kabilar ke fiskanta, suka kai harin wa jami'an tsaro. Sai dai 'yan kabilar ta Rohingya da yanzu ke ciki ugubar dakarun gwamnati, sun musanta ikirarin da aka yi cewa su ne suka fara kai hari wa jami'an tsaro. Kamfanin dillalcin labarai na AP ya ruwaito cewa dubban musluman 'yan kabilar ta Rohingya, aka ga suna ta isa Bangladesh a kafa, tsaffin da basa iya tafiya wasu an goyesu, yayin da aka ga yara na goye da jarirai. Mutanen dai basa dauke da komai illa tsumakaransu, inda suka bayyana cewa sun yi tafiyar akalla kwanaki uku kafin su isa kan iyakarsu da kasar Bangaldesh. Akallla dai akwai 'yan Rohingya da ke cikin ugubar rayu, bisa cin zali da gwamnati ke yi musu, kuma har yanzu hukumomin Myanmar basa yardan cewa yan kabilar ta Rohingya a matsayin yan kasa ne ba.