An bude yakin neman zab a Kwango Brazzaville
March 5, 2021Talla
An bude yakin neman zabe a Kwango Brazzaville a zaben shugaban kasar da za a gudanar a ranar 21 ga watan Maris wanda shugaba mai ci Denis Sassou Nguesso dan shekaru 77 wanda ya yi shekaru 36 a kan mulki, zai tsaya takara a wa'adi na hudu. A zaben da aka gudanar a shekara ta 2016 wanda Denis Sassou Nguesso ya samu nasara, tashin hankali ya barke bayan da 'yan adawa suka ce an yi aringizo a zaben.