1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Daukar ciki a makarantu na karuwa a Afirka

Mouhamadou Awal Balarabe
November 18, 2021

Batun kare hakkin ‘yan mata 'yan boko da ke fadawa cikin tsautsayin yin ciki a makaranta ko kuma wadanda ake yi wa auren wuri ko na dole suna na daga cikin muhimman batutuwa da wani taro ya duba a birnin Yamai na Nijar.

https://p.dw.com/p/43CD8
BG Schulen schließen und Schwangerschaften von Schülerinnen steigen in Kenia
Hoto: Monicah Mwagi/REUTERS

'Yan matan kasashen Afirka na fuskantar matsalar auren wuri da na dole tare da tsautsayin samun juna biyu a lokacin da suke tsakiyar karatu. Wadannan matsaloli na haifar masu da kyama a makarantu ko tsakanin sauran al’umma tare da tauye ‘yancinsu na samun ilimi. Sai dai kasancewar wannan kalubale ya zama ruwan dare a kasashe kamar Kamaru da Ghana da Najeriya, ya sa wani taro kwanaki uku da aka gudanar a birnin Niamye na Jamhuriyar Nijar ya dukafa kan wannan batu don samar da mafita.

kasar Kamaru na daya daga cikin kasashen Afirka da suka haramta wa mata dalibai masu dauke da ciki shiga makarantu, lamarin da ke jefa wadannan 'yan matan da iyayensu cikin damuwa. A Ghana kuwa, bangaren marasa rinjaye na majalisar dokokin kasar ya shawarci gwamnati da ta gaggauta goge tsarin karatu, saboda tsarin na haifar da mummunar sakamako a kan dalibai mata da suke yawaitan daukar ciki a makarantun sakandaren mata