1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Karfafa dangantaka da makwabta

Gazali Abdou Tasawa LMJ
September 30, 2021

Tawagar jami'an gwamnatin Aljeriya da kuma ta firaministan kasar Libiya na ziyarar aiki a Jamhuriyar Nijar, a wani mataki na karfafa huldar kasashen a fannonin diplomasiyya da tattalin arziki da kuma tsaro.

https://p.dw.com/p/415mc
Deutschland l Besuch des Nigerianischen Präsidenten in Berlin
Shugaban Jamhuriyar Nijar Mohamed BazoumHoto: Presse- und Kommunikationsdienst der Präsidentschaft von Niger

Tuni dai wasu al'ummar Jamhuriyar ta Nijar suka soma tofa albarkacin bakinsu, dangane da yadda kasar ke karfafa huldarta da kasashen Larabawa makwabtanta tun bayan hawan Shugaba Mohamed Bazoum karagar mulki. Bayan ganawar tawagar Aljeriyan da Shugaba Bazoum a fadarsa, ministan cikin gida na kasar ta Aljeriya Kamel Beldjoud ya bayyana cewa ziyarar tasu na da burin aiwatar da yarjeniyoyin da kasashen biyu suka cimma a ziyarar da Shugaban Nijar din ya kai a Aljeriyan a watan Yulin wannan shekara.

Libyen Parlament
Firaministan gwamnatin rikon kwarya ta Libiya Abdul Hamid DbeibehHoto: Libyan Government of National Accord/AA/picture alliance

A nata bangare tawagar jami'an gwamnatin Libiya ta isa Nijar a karkashin jagorancin firaministan rikon kwarya na kasar Abdul Hamid Dbeibeh. Firamnistan na Libiya dai ya share sa'o'i yana ganawa da Shugaba Bazoum a fadarsa, inda Nijar ta bayyana bukatar hadin kai tsakaninta da kasar ta Libiya wajen shawo kan matsalolin tsaron da take fuskanta. Tu dai bayan hawan Shugaba Bazouma kan karagar mulki watanni shidan da suka gabata, Nijar da ke da hulda ta kut da kut da makwabtanta, take neman karfafa dangantakarta da kasashen Larabawa da ke makwabtaka da itan. Yanzu haka dai tawagar ta jami'an gwamnatocin kasashen na Libiya da Aljeriya, na ci gaba da ziyarar tasu tare da ganawa da hukumomi dabam-dabam na Jamhuriyar ta Nijar.