Dambarwar kan belin Ibrahim El-Zakzaky | Zamantakewa | DW | 08.08.2019
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

Zamantakewa

Dambarwar kan belin Ibrahim El-Zakzaky

Gwamnatin Najeriya ta bai wa Sheikh Ibrahim El-Zakzaky izinin zuwa kasar Indiya don neman lafiya bayan da jagoran ya kwashi sama da shekaru 3 a tsare.

Wata kotu a jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya ce, ta bai wa jagoran Kungiyar 'yan Shi'a, Sheikh Ibrahim El-Zakzaky izinin zuwa kasar Indiya domin neman magani tare da mai dakinsa Zeena. Sai dai a yayin da hukumar tsaro ta farin kaya ta sanar da aiki da umurnin kotu bisa wasu sharruda da aka gindaya wa malamin, akwai batun lallai sai ya tafi da rakiyar jami’an tsaro, lamarin da yanzu haka ya haifar da cece-kuce a cikin kasar.

DW.COM

Sauti da bidiyo akan labarin