1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun kiyaye zaman lafiya sun mutu a Sudan ta kudu

Usman ShehuApril 9, 2013

A Sudan ta kudu an hallaka dakarun MDD masu aikin samar da zaman lafiya.

https://p.dw.com/p/18CRG
In this Thursday, July 14, 2011 photo released by the African Union/UN Hybrid operation in Darfur (UNAMID), UNAMID Rwandan troops escort returneesduring a repatriation operation for more than 200 displaced families returning from Aramba to their original village, Sehjanna, north Darfur, Sudan. After more than seven years in an internally displaced persons (IDP) camp in Aramba, near Kabkabiya, north Darfur, Sudan, they decided to participate at this voluntary repatriation program organized by UN Refugee Agency (UNHCR) and the Sudanese Humanitarian Aid Commission, with the logistical support of UNAMID. The families are farmers who fled their original village in Sehjanna (near Kutum, north Darfur) due to the conflict in Darfur. (Foto:UNAMID, Albert Gonzalez Farran/AP/dapd)
Dakarun MDD a SudanHoto: UNAMID/AP

An hallaka sojojin kiyayen zaman lafiya na MDD a Sudan ta kudu. rahotanni suka ce wasu mahara da ba a kai ga tantancewa ba, suka yi wa sojojin da ma'aikata farar hula na MDD kwantar ɓauna. Rundunnar kiyaye zaman lafiya ta MDD dake Sudan ta kudu wato a taƙaice UNMISS, ta tabbatar da harin, inda ta ce an kuma jikkaa wasu ojoji dama fararen hula, yayin kwantan ɓaunan da ya faru. Sai dai ba a ambaci asalin ƙasashen sojojin da aka hallaka da ke cikin rundunar kiyaye zaman lafiya a Sudan ta kudu.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Yahouza Sadissou Madobi