1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabannin kasashe sun halarci taro kan cutar COVID-19

Zulaiha Abubakar
May 4, 2020

Shugabannin kasashe hadin gwiwa da kungiyoyi da kuma bankuna sun bukaci kudaden da yawansu ya kai dala biliyan takwas domin gano rigakafin cutar Coronavirus.

https://p.dw.com/p/3blmb
Symbolbild Corona-Virus Impfstoff
Hoto: picture-alliance/dpa/Geisler-Fotopress

An gabatar da wannan bukata ne yayin babban taron da ya gudana ta bidiyo a wannan Litinin din, wanda kungiyar EU ta shirya. a lokacin wannan taro dai babu wakilcin kasashen Amirka da Rasha duk kuwa da cewar annobar ta Covid-19 tayi sanadiyyar mutuwar mutanen da yawansu ya kai 67,000 a Amirka .

Da yake jawabi a lokacin taron babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya jaddada muhimmancin hadin kai da bukatar yin watsi da gasa a wannan lokaci na laluben rigakafin COVID-19, bayan ya jaddada bukatar amfani da kudaden a bangaren samar da rigakafin da kuma gudanar da sabbin gwaje-gwaje.