1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cikas ga kokarin samar da zaman lafiya a Mali

July 18, 2013

Tashe-tashen hankula a cikin gida da Najeriya ke fama da su, ya sa hukumomin kasar janye dakarun kasar da ke Mali.

https://p.dw.com/p/19AU7
Nigerian soldiers part of Economic Community of West African States (ECOWAS) troops train on January 19, 2013 on the 101st airbase in Bamako. Ivorian President Alassane Ouattara on January 19 called for a broader international commitment to the military operations in Mali, where Malian and French forces are battling Islamist militant groups that control the country's vast arid north. Some 2,000 members of MISMA (the International Mission for Mali Assistance), the African intervention force, are expected to be deployed by January 26. About 100 soldiers from Togo and Nigeria have already arrived in Bamako, and another 30 or so from Benin are en route to join them. AFP PHOTO / ERIC FEFERBERG (Photo credit should read ERIC FEFERBERG/AFP/Getty Images)
Hoto: Eric Feferberg/AFP/Getty Images

Hukumomin Najeriya sun fadi - a wannan Alhamis (18.07.13) cewar, kasar za ta janye wasu daga cikin sojojinta da ke aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Mali. Ko da shike gwamnatin Najeriya ba ta bayyana dalilin daukar matakin ba, amma shugaban Kungiyar Gamayyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka, kana shugaban Cote d'Ivoire Alassane Ouattara, ya tabbatar da hakan a lokacin wani taron da shugabannin kungiyar ke ci gaba da yi a Abuja, fadar gwamnatin Najeriya. Shugaba Ouattara, ya ambata cewar, ya samu wasikar neman janye dakarun ne daga shugaba Jonathan na Najeriya, inda ya alakanta hakan da irin abubuwan da ke faruwa a cikin Najeriyar - kanta.

Dama dai Najeriya na da kimanin dakaru dubu daya ne a Mali, wadda ke kokarin farfado wa daga juyin mulkin soji a watan Maris na shekara ta 2012, bayan da wasu masu tada kayar baya suka kwace iko da yankin arewacin kasar. Ita kanta Najeriyar na fama da rigingimu musamman a yankin arewacin kasar, baya ga rikicin siyasar da ke neman kunno-kai a yankin da shugaban kasar ya fito.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe