1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ci gaba da takurawa 'yan jarida a Masar

June 28, 2013

Gwamnatin kasar Masar na ci gaba da matsawa 'yan jaridu, musamman wadanda ke nuna gazawar gwamnatin wajen biyawa talakawa bukatunsu.

https://p.dw.com/p/18y74
Hoto: Reuters

Shugaban kasar Masar Muhammad Mursi  ya bayyana rufe wata kafar yada labarai mai zaman kanata a kasar mai suna al-Faraeen, bisa zargin ta da yada labaran karya.

Haka nan ma wata kotu ta tuhumi mamallakin gidan talabijin na CBC Mohammed al-Amin, da laifin kin biyan haraji tare kuma da hana shi fita daga kasar, kwana guda bayan da Shugaba Mursi ya fito karara ya na sukansa.

A bangare guda kuma 'yan adawa a kasar na ci gaba da sukan gwamnatin Mursi, inda suke daukar gwamnatin a matsayin wadda take dakile ci gaba da kuma wargatsa kasar.

'Yan adawar dai sun shirya gudanar da wata gagarumar zanga-zangar kin jinin gwamnati a jibi Lahadi idan Allah ya kaimu, yayin da suma a nasu bangaren masu goyan bayan Shugaba Mursi suka shirya gudanar da zanga-zangar nuna masa kauna.

Maawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Umaru Aliyu