1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyoyin kasa da kasa na fuskantar kalubale a Burundi

Salissou Boukari
September 28, 2018

Gwamnatin kasar Burundi ta dakatar da ayyukan kungiyoyi masu zaman kansu na kasashen waje da ke ayyuka a kasarta har na tsawon watanni uku daga daya ga watan Oktoba mai zuwa.

https://p.dw.com/p/35f3A
Archivbild - Burundi's President Pierre Nkurunziza
Hoto: Reuters/E. Ngendakumana

Burundin ta dauki wannan mataki ne har lokacin da dokar da ta kayyade ayyukan kungiyoyin za ta soma aiki. bayan dai wani bincike ne da kwamitin tsaro na kasar ta Burundi ya gudanar kan ayyukan kungiyoyin, ya gano cewa akasarin kungiyoyin ba su bin dokokin kasar ta Burundi kaman yadda babban sakataran gudanarwa na kwamitin tsaron Janar Sisas Ntigurirwa ya sanar yayin wani jawabi da ya yi ta gidan talbijin na kasar ta Burundi, wanda ya ce sake komawar kungiyoyin kan ayyukansu zai ta'allaka ne ga yadda suka aminta da sabuwar dokar. Sai dai tuni wasu jam'an diflomasiyya ke nuna shakkunsu kan lamarin na ganin wannan sabon mataki na da gwamnatin ta Burundi ta dauka ka iya sanya wasu kungiyoyin su rufe ma'aikatunsu a kasar.