1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mayakan jihadi sun halaka mutum 37

Ramatu Garba Baba
November 7, 2019

Masu aikin hakar ma'adanai kimanin 37 ne suka halaka a sakamakon wani harin kwanton bauna da mayakan jihadi suka kai kan ayarinsu a wani yanki mai suna Tapoa.

https://p.dw.com/p/3SbFf
Burkina Faso Nach den Anschlägen
Hoto: Getty Images/AFP/A. Ouoba

Shugaban kamfanin da mallakin wasu 'yan Kanada ne , ya ce, akwai tagawar jami'an tsaro da ke rakiyar ma'aikatan a yayin harin, sai dai wani jami'in tsaron kasar ta Burkina Fason, ya ce motocin sun taka abubuwan fashewa da mayakan suka riga suka dasa ne a kan hanyar. Gwamnatin kasar mai fama da tashe-tashen hankula daga masu tayar da kayar baya a kasashen yankin Sahel, ta ce harin ya kasance mafi muni da kasar ta fuskanta a cikin shekaru biyar. Semafo mallakin wasu 'yan kanada ne da ke da kamfanonin hakar ma'adanai biyu a cikin kasar. A safiyar jiya Laraba aka kai harin da ya kara tayar da hankula al'umma a yankin.