1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaba Buhari na fuskantar barazanar tsigewa

July 28, 2022

Bayan tsawon lokaci na biyayya da ya kai ga zargin majalisu da fadawa aljihun 'yan mulki, shugaban Najeriya da 'yan majalisu na shirin gwada kwanji a rikicin rashin tsaro da ya kai ga barazanar tsige Muhammadu Buhari.

https://p.dw.com/p/4ElzD
Muhammadu Buhari, Präsident von Nigeria
Matsalar tsaro na barazanar ga mulkin Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya Hoto: Siphiwe Sibeko/REUTERS

'Yan majalisun tarrayar Najeriya biyu sun rika biyan bukatar gwamnatin kasar a kusan ko yaushe, lamarin da ya kai ga zarginsu da fadawa aljihun 'yan mulkin kasar. Sai dai danyen ganyen na shirin karewa, inda 'yan majalisun suka bai wa shugaban kasar wa'adin makonni shida na kawo karshen rikicin rashin tsaron kasar ko kuma ya fuskanci barazanar tsigewa. Wannan ne dai karo na farko a shekaru uku da doriya da majalisun ke nuna wa shugaban kasar jan kati bisa rawar da yake takawa a harkar ta tsaro.

Matsayin bangaren 'yan adawa da masu mulki

Duk da cewa  jam'iyyun adawa a majalisar dattawa ta kasar ne suka fara wannan yunkuri, amma barazanar tsigewar ta yadu zuwa 'yan jam'iyyar APC ta shugaban kasar. Yusuf Shitu Galambi, dan majalisar wakilai daga jam'iyyar APC mai mulki, ya ce babu alamun gaskiya bisa rawar Buhari ga kokarin warware matsalar ta tsaro.

Daga dukkan alamu, sabuwar barazanar na shirin yamutsa lamura cikin kasar da ke fuskantar jerin rigingimu iri-iri a halin yanzu. Wata sanarwar fadar gwamnatin Najeriya ta kira rawar 'yan dokar da sunan wasan yara.Lai Mohammed, ministan labarai na kasar kuma kakakin gwamnatin kasar ya ce: " Ba batu ba ne da shugaban kasa ke yi wa rikon sakainar kashi, amma dai ba zan iya shaida muku matakan da gwamnati ke dauka a kan batun rashin tsaro ba. Ga masu wannan barazanar tsige shugaban kasa, ina jin ya fi kama da farfaganda, kuma abu ne na dariya."

Nigeria | Informationsminister Lai Mohammed
Lai Mohammed ya danganta yunkurin tsige Buhari da farfagandaHoto: picture-alliance/dpa/K. Wigglesworth

Me kundin tsrain mulkin Najeriya ya tanada ?

Duk da cewa an sha barazanar tsige shugabannin kasar, amma har ya zuwa yanzu babu tarihin iya kaiwa ga tsige shugaban kasa a tarrayar Najeriya. Kundin tsarin mulkin kasar ya tanadi ratabba hannun kashi biyu a cikin uku na masu doka ta kasar kafin a iya kaiwa ga fara babban aikin tsige shugaban kasar.Faruk BB Faruk da ke sharhi kan siyasa ta kasar ya ce da kamar wuya a tsige shugaban kasa a tarrayar Najeriyar saboda jam'iyyar APC na takama da rinjaye babba a majalisa.

Nationalversammlung in Abuja, Nigeria
Majalisun Najeriya na zargin gwamnatin tarayya da gaza magance matsalar tsaroHoto: cc-by-sa/Shiraz Chakera

Majalisar tsaron kasar na shirin dorawa a wani taron neman mafitar rikicin da ke nuna alamun wucewa da sanin 'yan mulkin Najeriya.