1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Hadarin jirgin ruwa ya rutsa da bakin haure

Ramatu Garba Baba
December 14, 2022

Firaiministan Britaniya Rishi Sunak ya baiyana takaicinsa kan asarar rayuka na wasu bakin haure da suka gamu da ajalinsu a sakamakon hadarin jirgin ruwa a mishigin kasar.

https://p.dw.com/p/4KvMx
Hoto: Peter Nicholls/REUTERS

Firaiministan Britaniya Rishi Sunak, ya baiyana bakin cikinsa a gaban majalisar kasar, kan asarar rayuka da aka samu a sakamakon wani hadarin jirgin ruwa da ya rutsa da wasu bakin haure.

Da asubahin wannan Laraba, aka ja hankalin jami'an da ke aikin tsaron gabar ruwan kasar da ta hade Britaniya da Faransa kan hadarin da karamin kwale-kwalen da ya debo wasu bakin haure ya yi, daga bisani jami'an sun iya gano gawarwakin wadanda suka mutu da kuma wasu wadanda suka tsira da rayukansu.

Masu fasakwabrin jama'a, sun jima suna amfani da kananan kwale-kwale makamancin wanda ya yi wannan hadarin, don shigar da bakin haure Britaniya ta barauniyar hanya, duk kuwa da kwararan matakan da gwamnatin kasar ke dauka na kare iyakarta daga bakin da ke jefa rayuwarsu a cikin hadari da zummar neman mafaka a Britaniyan.