1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Brexit: EU ta ce bakin alkalami ya bushe

Abdullahi Tanko Bala
February 7, 2019

Kungiyar Tarayyar Turai ta shaida wa Firaministar Birtaniya Theresa May cewa batun sake tattaunawa kan wata sabuwar yarjejeniya ta ficewar Birtaniya daga kungiyar EU ba zai yiwu ba.

https://p.dw.com/p/3Cunu
Großbritannien | Theresa May in  Belfast
Hoto: picture-alliance/dpa/Photoshot

Shugagaban hukumar tarayyar Turai Jean Claude Yuncker ya shaidawa Firaministar Birtaniya Theresa May cewa kungiyar EU ba za ta bude wata sabuwar tattaunawa da Birtaniya kan yarjejeniyar Brexit ta ficewar Birtaniya daga kungiyar EU ba.

Sai dai yace suna iya duba yiwuwar yin wasu 'yan gyare gyare kan yarjejeniyar da suka cimma a baya.

Juncker yace kasashe 27 na kungiyar tarayyar Turan suna nan akan matsaya guda game da yarjejeniyar da suka cimma da Birtaniya.

A sanarwar da ya fitar bayan ganawarsa da Theresa May a wannan Alhamis din a birnin Brussels Jean Claude Juncker yace dukkan wata matsaya da za a cimma wajibi ne sai ta sami amincewar majalisar dokokin Turai da kuma daukacin kasashen 27 na tarayyar Turai.