1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boran sojoji a Cote d'Ivoire

January 6, 2017

Tsofin 'yan tawaye wadanda suka goyi bayan Alassane Ouattara wadanda aka saka cikin rundunar sojojin kasar na yin zanga-zanga.

https://p.dw.com/p/2VPBU
Elfenbeinküste nach dem Anschlag
Hoto: Getty Images/AFP/S. Kambou

An ba da rahoton cewar an ji duriyar manyan makamai a birnin na biyu mafi girma na Cote d'Ivoire watau Bouake a kusa da barakin sojoji.Masu aiko da rahotanni sun ce tsofin sojojin wadanda suka ce suna bukatar ko wane a bashi kusan Euro dubu bakwai da rabi na kudaden alawus da kuma gidan kwana,sun kai farmaki a kan wasu ofisoshin 'yan sanda guda biyu inda suka amshe makamai daga 'yan sandar wadanda suka tafi da su.