Bom ya kashe sojojin kasar Mali
September 28, 2018Talla
Hukumomi a Mali sun tabbatar da mutuwar wasu sojojin kasar bakwai da wani direba farar hula guda, bayan wani tuntube da suka yi da wata nakiya a yankin tsakiyar kasar da ke fama da hare-haren ta'addanci.
Al'amarin da aka ruwaito shi a ranar Alhamis, ya faru ne a arewacin birnin Timbuktu da kuma Mopti, lokacin da sojojin ke rakiyar wani ayari.
A ranar ta Alhamis ne kuma wasu dakarun Faransa 120 suka dira a yankin arewa maso gabashin Malin mai makwabtaka da Jamhuriyar Nijar, don yaki da ayyukan 'yan ta'addan.
Dakarun na Faransa dai sun ce suna shirin ba da mamaki ne a yankin, ta hanyar gama karfi don yaki da masu ayyukan na tarzoma.