1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta yanka manoma a Borno

November 20, 2017

Mayakan Boko Haram sun kashe mutane shida ta hanyar yi masu yankan rago, a kauyen Dimge 'yan tazarar da Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno.

https://p.dw.com/p/2nw9a
Wasu mazauna wajen birnin Maiduguri a Najeriya
Wasu mazauna wajen birnin Maiduguri a NajeriyaHoto: DW/A.Kriesch

Wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne sun kashe mutane shida ta hanyar yi masu yankan rago, a kauyen Dimge 'yar tazara da birnin Maiduguri fadar gwamnatin jihar Borno. Lamarin ya faru ne a jiya Lahadi,  yayinda manoman ke aiki a gonakinsu.

Maharan na Boko Haram su bakwai bisa babura sun sun afka wa manoman ne, sannnan suka kyale wani dattijo don ya kai labari, kamar yadda wani dan kato-da-gora ya tabbatar. Wannan hari ya tayar da hankulan manoma da suka kauracewa gonakinsu, kamar yadda 'yan uwan wadanda aka yanka suka bayyana.

Ya zuwa yanu dai jami'an tsaro ba su ce komai kan wannan hari ba, kuma ba a kaiga daukar gawarwakin mamatan ba.