Boko Haram ta kashe mutane 10 a Kamaru
August 7, 2014Talla
Wani babban jami'in gwamnatin ƙasar ta Kamaru ya ce wani gungun ne, na mahaharan suka datse hanyar mota a garin Zigague. Kana suka tare wata babbar motar da ke ɗauke da farar hula guda tara da soji ɗaya waɗanda suka buɗewa wuta nan take suka hallakasu.
Wannan hari, ya biyo bayan sace mai ɗakin mataimakin firaministan ƙasar ta Kamaru, da wasu mutane 15 da Ƙungiyar Boko Haram ta yi a makon jiya a arewacin ƙasar ta Kamaru.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu