1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kama mata a Nijar

Yusuf Bala Nayaya
July 4, 2017

Harin dai an kai shi ne a ranar Lahadi a kauyen na Ngalewa da ke kusa da iyaka da Najeriya kamar yadda gwamnan Diffa Laouali Mahamane Dan Dano ya bayyana haka.

https://p.dw.com/p/2ftsU
Afrika - humanitäre Hilfe im Tschadsee-Gebiet
Hoto: picture-alliance/AP Photo/A. Harnik

Mayakan Boko Haram sun sace mata 37 da yanka makogwaro na wasu mutane a wani kauye da ke a Kudu maso Gabashi na Jamhuriyar Nijar kamar yadda gwamna a yankin ya bayyana a wannan rana ta Talata. Harin dai an kai shi ne a ranar Lahadi a  kauyen na Ngalewa da ke kusa da iyaka da Najeriya kamar yadda gwamnan Diffa Laouali Mahamane Dan Dano ya bayyana wa kafar yada labarai a jihar.

A cewar gwamnan tuni jami'an tsaro suka shiga aiki na bincike inda mayakan na Boko Haram suka tafi da matan don samar musu 'yancinsu.

A cewar magajin garin na  Ngalewa El Hadj Daouda, yayin tattaunawa da kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP  an kai hari a garin ne a ranar Lahadi da misalin karfe goma zuwa sha daya na dare.