1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

'Yan matan Chibok: sama da mata 20 sun yi aure da Boko Haram

June 22, 2022

'Yan matan Chibok biyu da sojoji suka ceto ne suka shaida wa 'yan jarida yadda Boko Haram ta yi musu auran dole. A cikin daji ne dai sojojin suka samu matan, kowacce da karamin yaron da ta haifa wa dan Boko Haram.

https://p.dw.com/p/4D2o5
Stephanie Sinclair - Gewinnerin des Anja Niedringhauspreis 2017
Hoto: IWMF/Stephanie Sinclair

Rundunar sojin Najeriya ta gano tsaffin dalibai mata na makarantar sakandaren Chibok ta jihar Borno da ke cikin 'yan mata 276 da kungiyar Boko Haram ta kwase shekaru takwas da suka gabata. 


A yayin da yake gabatar da matan a Maiduguri, Manjo Janar Christopher Musa, wani babban jami'in sojin Najeriya  ya ce a wurare dabam-dabam sojoji suka yi nasarar samun matan a makon da ya gabata. 


Mary Dauda da sojojin suka gan ta a cikin daji ta ce kawo yanzu Boko Haram ta aura wa mambobinta sama da matan Chibok 20 da ta baro. Ta ce mayakan Boko Haram kan lakada musu duka idan ba su yi sallah ba. Ita kuma Hauwa Joseph ta ce dan Boko Haram din da ya aure ta ya mutu a yayin wani gumurzu da sojojin Najeriya. Ta ce bayan mutuwarsa mambobin kungiyar sun yi watsi da ita da karamin yaron da ta haifa.