1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram: Soji sun shiga dajin Sambisa

Ahmed SalisuApril 22, 2015

Dakarun Najeriya sun kutsa dajin nan na Sambisa a wani abin da sojin ke cewa fafatawa ce ta karshe da suke sa ran yi da 'yan kungiyar Boko Haram.

https://p.dw.com/p/1FDDM
Nigeria Kampf gegen Boko Haram Islamisten
Hoto: picture-alliance/AP

Dakarun na Najeriya na kasa da ma mayakan sama, su ne dai rahotannin suka tabbatar da dannawarsu cikin dajin a Larabar ta yau.

Sai dai ya zuwa wannan lokacin babu wani sakamako dangane da dauki-ba-dadin da ya wakana a arangamar da ake ganin za ta hada da kubuto da 'yan matan makarantar Chibok sama da 200 da ke hannun mayakan yau sama da shekara guda kenan.

A watannin baya ma dai sojojin Kamaru da Chadi da ma Jamhuriyar Nijar, sun zafafa hare-hare kan mayakan na Boko Haram, a kokarin murkushe su saboda fadada hare-hare da kungiyar ta yi zuwa ketaren Najeriyar.