1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyar Labour a Birtaniya za ta shiga zabe

Mohammad Nasiru Awal AH
October 29, 2019

Tun farko dai jam'iyyar Conservative ta Firaminista Boris Johnson na son a gudanar da sabon zabe a ranar 12 ga watan Disamba na wannan shekara.

https://p.dw.com/p/3S8jx
Großbritannien Jeremy Corbyn Labour
Hoto: Reuters/N. Hall

Shugaban jam'iyyar Labour a Birtaniya Jeremy Corbyn ya tabbatar cewa jam'iyyarsa ta hamaiya ta janye adawar da take ga gudanar da sabon zabe na gaba da wa'adi, bayan da Kungyar Tarayyar Turai ta ba da karin lokaci na watanni uku kan ficewar Birtaniya daga kungiyar.

Corbyn ya ce za su yi nasara a zaben da bisa ga dukkan alamu zai gudana cikin watan Disamba mai zuwa.

Ya ce: "Mun shirya mu yi zabe. Za mu fita da gagarumin sako yadda za mu canja al'ummarmu don kawo karshen rashin daidaito da rashin adalci. Za mu tinkari matsalar talauci da da yawa daga cikin mutane ke fuskanta. Lalle muna son zaben, amma kuma muna son a cire maganar ficewar Birtaniya daga EU ba tare da yarjejeniya ba."

Ita dai jam'iyyar Conservative ta Firaministan Birtaniya Boris Johnson na son a gudanar da sabon zabe a ranar 12 ga watan Disamba na wannan shekara ta 2019.