Biden: Trump na barazana ga dimukuradiyya
September 2, 2022Joe Biden ya tuhumi Donald Trump da jiga-jigan magoya bayansa da hali irin na tsatstsauran ra'ayi da ke barazana ga harkokin siyasa da dimukuradiyyar Amirka, yana mai kira ga dukkan 'yan kasar su taimaka wajen dakile bara gurbi da ke cikin jam'iyyar Republican.
Da yake jawabi a zauren shelar ‘yancin Amirika a birnin Philadelphia na jihar Pennslavania, Shugaba Joe Biden yana cewa "Ba zan tsaya kallo ba, a soke nufin jama'ar Amirka ta makirci da hujjoji marasa tushe da da'awar zamba. Ba zan bari mutanen da suka yi yarda sun fadi zabe su saci kuri'u ba. Ba zan tsaya ina kallon mafi girman 'yanci a wannan kasa, 'yancin kada kuri'a da aka kirga a karbe su ba. A matsayina na shugaban ku, zan kare dimokuradiyyar mu da kowane zarafi na raina. Kuma ina rokon kowane Ba'amurke ya shiga tafiyar.