1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karfafa hulda tsakanin Rasha da hukumomin Bangui

Salissou Boukari
August 21, 2018

A wannan Talatan ce kasar Rasha da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya suka saka hannu kan wata yarjejeniya da za ta ba da damar horas da sojojin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.

https://p.dw.com/p/33WPL
Symbolbild Militär in Burundi
Hoto: S. Kambou/AFP/Getty Images

Hakan na zuwa ne 'yan kwanaki da kashe wasu 'yan jaridar kasar ta Rasha a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya wanda ya nunar a fili irin huldar da ke tsakanin kasashen biyu. Da yake magana bayan rattaba hannu kan yarjejeniyar tare da takwararsa Marie-Noëlle Koyara ta Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, ministan tsaron kasar  Rasha Sergueï Choïgou, ya ce burin shi ne na karfafa huldar tsaro tsakanin kasashen biyu.

Tun dai a farkon wannan shekara kasar Rasha ta aike da manyan sojojinta guda biyar tare da fararan hulla 170 masu bada horo, sannan kuma ta bayar da makammai ga gwamnatin kasar bayan da ta samu izini daga Majalisar Dinkin Duniya.