Bukatar inganta ilimin mata a Afirka
July 8, 2019Talla
A wata hira da ta yi da wakilinmu na Yamai fadar gwamnatin Jamhuriyar Nijar Mahaman Kanta a gefen taron kungiyar Tarayyar Afirka AU, Amina J. Mohammed da kuma ke zaman 'yar siyasa daga Tarayyar Najeriya, ta yaba da tsarin kasuwanci mara shingen da kasashen Afirkan suka kaddamar tare kuma da bukatar gaggauta tallafawa ilimin yara mata.