1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bama ba ta son a binciketa

Abdourahamane Hassane
December 20, 2017

Hukumomin kasar Bama sun haramta wa kakakin musammun ta MDD isa kasar domin tantance gaskiyyar abin da ya faru.

https://p.dw.com/p/2pi1S
 Yanghee Lee Kakakin Majalisar Dinkin Duniya
Yanghee Lee Kakakin Majalisar Dinkin DuniyaHoto: picture-alliance/EuropaNewswire/L. Rampelotto

A cikin wata sanarwa da ta bayyana kakakin ta Majalisar Dinkin Duniya Yanghee Lee ta ce abin kunya ne haramcin da kasar ta Bama ta yi ma ta na shiga kasar, kuma hakan na nufin akwai wani abin da hukumomin na Bama ke boyewa. Fadan da aka yi tsakanin sojojin kasar ta Bama da 'yan kabilar Rohingya a yankin  Rakhine da ke a yammacin kasar a cikin watan Augusta da ya gabata. Ya yi sanadiyyar mutuwar rayukan jama'a da dama yayin da wasu suka fice daga matsugunansu.