Bama ba ta son a binciketa
December 20, 2017Talla
A cikin wata sanarwa da ta bayyana kakakin ta Majalisar Dinkin Duniya Yanghee Lee ta ce abin kunya ne haramcin da kasar ta Bama ta yi ma ta na shiga kasar, kuma hakan na nufin akwai wani abin da hukumomin na Bama ke boyewa. Fadan da aka yi tsakanin sojojin kasar ta Bama da 'yan kabilar Rohingya a yankin Rakhine da ke a yammacin kasar a cikin watan Augusta da ya gabata. Ya yi sanadiyyar mutuwar rayukan jama'a da dama yayin da wasu suka fice daga matsugunansu.