1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bakin haure sun rasa rayukansu a Yemen

June 14, 2021

Jami'an Majalisar Dinkin Duniya da na Yemen na cewa akalla bakin haure 200 wanda yawancinsu suka fito daga kasashen Afirka sun yi batan dabo, kwana guda bayan da kwale-kwalensu ya kife a gabar ruwan Yemen.

https://p.dw.com/p/3uuNz
Jemen Migranten
Hoto: AFP/IOM

Kifewar kwale-kwalen na kasancewa mafi munin hatsari na baya-bayan nan da ya rutsa da bakin hauren da suka fito daga nahiyar Afirka don neman rayuwa mai inganci a kasashen yankin Gulf masu arzikin man fetur.

Rahotanni na nuna cewa kwale-kwalen ya taso ne daga kasar Jibuti dake gabashin Afirka inda ya nutse a yankin Ras al-Ara da ke lardin Lahj na kasar Yemen. Sai dai har kawo yanzu babu rahoton da ya ce wasu sun rasa rayukansu ko ma an ceto wasu. Ko a watan Afrilun da ya gabata wani kwale-kwale dauke da bakin haure 40 ya kife a gabar ruwan Jibuti.

Dubban mutane ne dai ke gujewa talaunci a kasashen Habasha da Jibuti da Somaliya zuwa Yemen don tsallaka wa zuwa kasashen yankin Gulf.