1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

Asusun IMF ya yafe wa kasashen Afirka bashi

October 8, 2021

Asusun ya yafe wa kasashen da ke fama da tarnakin corona kudaden da suka ranto. Kudade ne dai da ake sa ran za su taimaka wa kasashen fita daga halin da suka shiga.

https://p.dw.com/p/41Sk4
IWF Report Logo
Hoto: Yuri Gripas/REUTERS

Asusun ba da lamuni na duniya IMF, ya fitar da sunayen wasu kasashe matalauta 24 wadanda zai yafe wa basukan da yake bin su, domin ba su damar warware matsalolin da suka shiga saboda corona.

IMF ya ce basukan da yake yafewa a karo na hudu saboda coronar, sun kai na miliyan 973 na dala, kari kan miliyan 124 da ya yi tun da fari.

Kasashen dai sun hada har da wadanda suka ranto kudade a baya-bayan nan wato Lesotho da Kyrgystan.

Wasu kasashen sun hada da Benin da Burkina Faso da Mali da Nijar da kasashen Guinea Conakry da Guinea Bissau da Tsibirin Comoros.

Haka ma akwai kasashe irin su Gambiya da Burundi da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da Habasha da Laberiya da Haiti da kasar Malawi.