1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Aqmi ta ɗauki alhakin hare/haren Cote d'Ivoire

Abdourahamane HassaneMarch 14, 2016

Mutane guda 14 suka rasa rayukansu yayin da wasu 22 suka jikkata a harin da wasu yan bindiga suka kai a Grand Bassam

https://p.dw.com/p/1ICc3
Elfenbeinküste Anschlag Grand Bassam in Abidjan
Hoto: Reuters/J. Penney

Kungiyar Aqmi reshen Ƙungiyar Al-Qaida a yankin Magreb ta ɗauki alhakin kai harin da wasu 'yan bindigar guda shida suka kai a jiya a wani otel da ke a Grand Bassam a Kudancin Cote d'Ivoire.

Mutane guda 14 suka mutu akasari fararan hula a ciki har da wasu 'yan ƙasashen Faransa da Jamus da kuma Birtaniya da kuma wasu sojoji biyu yayin da wasau 22 suka jikkata.Wannan shi ne dai karo na uku da yan bindiga ke kai hare-haren na ta'addancin yammacin Afirka bayan Mali da Burkina Faso