1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana zaben yankuna a kasar Kamaru

December 6, 2020

Gwamnatin kasar Kamaru, na gudanar da zaben majalisun yankunta a karon farko a yau Lahadi. Yankunan Kamarun 10 ne dai ciki har da biyu da ke a yankin renon Ingila

https://p.dw.com/p/3mHeA
Kamerun Wahlen
Hoto: picture-alliance/Xinhua/J. P. Kepseu

Sama da shekaru 20 ne dai kundin tsarin mulkin ya bayar da damar zaben na yankuna, to sai dai a wannan karon ne ake iya cewa 'yan kasa za su gani.

A karshen shekarar da ta gabata ne, Shugaba Paul Biya, ya yi alkawarin zaben a kokarin kwantar da wutar rikicin ‘yan aware da ke ruruwa a yankin renon Ingila na kasar.

Manufar hakan kuwa shi ne domin bai wa yankin karin ikon mulki musamman ma a kan batutuwan da suka shafi al’umomin da ke zaune a cikinsa.

Sai dai kuma a bayyane yake, galibin mazauna yankin dai ba su da kwarin gwiwa a wannan zabe na yau.