An samu wasu sojoji da laifin aikata kisan jama'a a Kamaru
June 11, 2020Talla
Kakakin rundunar sojojin na Kamaru Cyrille Atonfack Guemo ya ce ana tsare da sojojin a gidan yari na soja na birnin Yaounde. An dai samu sojojin guda uku da laifin kashe farar fula 23 a ciki har da yara kankana guda goma a cikin watan Maris da ya gabata a Ngarbuh da ke a arewa maso yammacin Kamarun.