1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana tattaunawa kan nukiliyar Iran

June 17, 2014

Iran ta sake komawa tattaunawa kan batun nikiliyar kasar da sauran kasashen Yammacin Duniya

https://p.dw.com/p/1CKlV
Hoto: Reuters

Kasar Iran da kasashen Yamma da ke halartan tattaunawa kan sasanta batun makamashin kasar sun fara wani zagayen tattaunawa. Shugabannin suna lalubo hanyar da za bi domin samun matsaya, ta yadda za a kawo karshen takaddamar mallakar nukiliyar kasar Iran

Kungiyar Tarayyar Turai ke jagorantar tattaunawa, inda ake sa ran sassautowa daga kowane bangare yayin da aka zo rubuta tankardar karshen ganawar, wadda ke babban cikas da ake samu.

A yanzu haka wasu kasashen yamma sun fara sassautawa kan adawar da suke nuna wa Iran, inda tuni kasar Birtaniya ta sanar da sake bude ofishin jakadancin kasar ta Iran, wanda ke nuna aluman yarda da juna tsakaninsu da Iran.

Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Suleiman Babayo