1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana tattaunawa a Burkina Faso

Abdourahamane HassaneNovember 5, 2014

Shugabannin ƙasashen Najeriya da Senegal da kuma na Ghana na tattaunawa da Lt. Col. Isaac Yacouba Zida

https://p.dw.com/p/1DhAA
Burkina Faso - Oberst Isaac Zida
Hoto: ISSOUF SANOGO/AFP/Getty Images

Shugabannin guda uku waɗanda suka isa a birnin Ouagadougou na tattaunawa a asirce da mutumin wanda ya yi ikirarin kansa a matsayin shugaban gwamnatin ruƙon kwarya na ƙasar.

Bayan faɗuwar gamnatin Blaise Compaore a makon jiya wanda ya shafe shekaru 27 a kan karagar mulki.Shugabanin guda uku wato Macky Sall na Senegal da Goodluck Jonathan na Najeriya da kuma John Dramani Mahama na Ghana. Wanda shi ne shugaban Ƙungiyar ECOWAS. za su yi ƙoƙarin shawo kan shugaban riƙon na Burkina Faso da ya miƙa mulki ga hannun farar hulla.