1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Myanmar: Ana ci gaba da aiwatar da kisan kare dangi

Ramatu Garba Baba
October 25, 2018

A wani bincike da Majalisar Dinkin Duniya ta gudanar, ta ce ta gano yadda har yanzu ake ci gaba da samun kashe-kashe na 'yan kabilar Rohingya da suka yi saura a jahar Rakhine na kasar Myanmar.

https://p.dw.com/p/37A5p
Bangladesch Rohingya Flüchtlings Camp
Hoto: DW/I. Pohl

Marzuki Darusman wakilin majalisar a kasar, ya ce matsalar babba ce, kuma har yanzu dubban 'yan Rohingya ne ke tururuwa suna tserewa gidajensu bisa wannan barazana da suke fuskanta, wadanda suka zabi zama kuwa suna fuskantar matsaloli na musgunawa da kaskanci daga jami'an gwamnati inji sanarwar.

A wani taron manema labarai, mista Darusman ya ce, ba a daina aikata laifi na kisan kare dangi ba akan 'yan tsirarun da ke zaune a  jahar Rakhine a arewacin kasar. Amma Jakadan Myanmar a Majalisar Dinkin Duniyan,  Hau Do Suan, ya karyata sakamakon wannan binciken inda ya ce an nuna bangaranci da rashin adalci ga gwamnatin Myanmar. Dubban 'yan kabilar Rohingya ne suka rikide zuwa 'yan gudun hijira bayan da kazamin rikicin kabilanci ya barke a kasar.