1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zargi kungiyar IS da aikata kisan kare dangi

Mohammad Nasiru AwalMarch 19, 2015

Majalisar Dinkin Duniya ta ce hare-haren da 'yan IS ke kai wa a kan mabiya tsirarun addinai sun yi daidai da kisan kiyashi.

https://p.dw.com/p/1EtEH
Jesidische Flüchtlinge im Irak 20.08.2014
Hoto: picture-alliance/abaca/Depo Photos

Majalisar Dinkin Duniya ta ce 'yan ta'addar kungiyar IS na aikata kisan kare dangi da kuma ta'asar laifin yaki. Wani rahoto da babbar hukumar kare hakin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya ta fitar a birnin Geneva ya ce hare-haren da 'yan IS ke kai wa a kan mabiya tsirarun addinai sun yi daidai da kisan kiyashi. Rahoton ya kuma zargi sojojin Iraki da aikata munanan laifuka. Mawallafan rahoton sun yi kira da a mika wannan batu ga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa da ke birnin The Hague.