1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sahle-Work ta zama shugabar kasar Habasha

Abdul-raheem Hassan
October 25, 2018

Da gagarumar rinjaye 'yan majalisar dokokin Habasha sun zabi Sahle-Work Zewde a matsayin mace ta farko da za ta jagoranci kasar a matsayin shugaba.

https://p.dw.com/p/37C3Y
Äthiopien Addis Abeba neue Präsidentin Sahle-Work Zewde
Hoto: Getty Images/AFP/E. Soteras

Zaben Sahle-Work na zuwa ne mako guda bayan da firaiminista Abiy Ahmed ya nada mata da dama cikin sabbin ministocin gwamnatinsa.

Sabuwar shugabar mai shekaru 68 ta yi aiki a Majalisar Dinkin Duniya. Sahle-Work za ta maye gurbin tsohon shugaban kasar Mulatu Teshome wanda ya yi murabus daga mukamin.

Sahle-Work ta yi alkawarin aiki tukuru wajen tabbatar da hadin kan al'ummar Habasha a wani yunkuri na kawo zaman lafiya a kasar da ke fama da rikicin kabilanci.