1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An zaɓi mace ta farko a shugabancin Koriya ta kudu

Usman ShehuDecember 20, 2012

Ƙalubalen tsaro da tattalin arziki sune a gaban Geun-Hye Park sabuwar shugabar Koriya ta kudu, wanda ta lashe zaɓen shugaban ƙasar

https://p.dw.com/p/176GP
South Korea's presidential candidate Park Geun-hye of the ruling Saenuri Party waves to supporters during her presidential election campaign in Suwon, south of Seoul, South Korea, Monday, Dec. 17, 2012. South Korea's presidential election is scheduled for Dec. 19. (Foto:Lee Jin-man/AP/dapd)
Park Geun-Hye, sabuwar shugabar Koriya ta kuduHoto: dapd

A ƙasar Koriya ta kudu, karo na farko an zaɓi mace a matsayin shugabar ƙasa, Geun-Hye Park yar tsohon shugaban ƙasar Koriya ta kudu a zamanin mulkin soji, mahaifin na ta Park Chung-Hee a tsawon mulkinsa ya maida hankali ne bisa inganta tattalin arzikin ƙasar da kuma kare ta daga barazanar maƙobciyarsu kana abokiyar gaba wato Koriya ta arewa.

A jawabin bayan nasarar zaɓe da ta yi wa yan ƙasar, Park ta fito a fili ta bayyana cewa babban abinda za ta sa a gaba shine batun tsaro, inda ta ce harba makaman roka da Koriya ta arewa ta yi makwannin da suka gabata, wata babbar barazanace da ba za gyale ba. Don haka ta shaida wa yan ƙasar cewa "zan cika alƙawari da na yi muku na ƙarfafa tsaron ƙasar mu da kuma faɗaɗa matakan difalmasiyya"

North Korean leader Kim Jong Un, right, salutes a mass military parade in Pyongyang's Kim Il Sung Square to celebrate 100 years since the birth of his grandfather and North Korean founder, Kim Il Sung on Sunday, April 15, 2012. Kim delivered his first public televised speech Sunday, just two days after a failed rocket launch, portraying himself as a strong military chief unafraid of foreign powers during festivities meant to glorify his grandfather, North Korea founder Kim Il Sung. (Foto:Ng Han Guan/AP/dapd)
Man'yan jami'an gwamnatin Koriya ta arewa ke kallo paretin sojiHoto: AP

A lokacin yaƙin neman zaɓen ta Geun-Hye Park, ta nisanta kanta da tsarin shugaba mai barin gado, wanda ya yanke duk matakan bai wa Koriya ta arewa tallafin jinƙai. A wani ɓangaren nuna manufofinta kan yankin Asiya, Park ta jaddada cewa za ta maida hankali wajen inganta tsaro a gabashin Asiya, inda yanzu haka ake taƙaddama tsakanin ƙasashen Koriya ta kudu, Japan da China bisa mallakar wasu tsibirai.

Hong Hyun-Il dake cibiyar nazarin al'amuran yau da kullum a gabashin Asiya, yace sanin halayen matar da kuma matsayin jam'iyarta, za a samu sauyi bisa dangantakarsu da Koriya ta arewa, koda yake amma abune mai yuwa ta kasance shugabar farko da za ta sasanta da Koriya ta arewa.

Kawo yanzu dai ƙasar China wanda itace ƙasa ɗaya tilo a yankin Asiya mai ɗasawa da Koriya ta arewa, ta taya sabuwar shugabar koriya ta arewa murna. A safiyar yau Park ta kai ziyara kan kabarin mahaifinta Park Chung-Hee stohon shugaban mulkin soja, kana daga bisani ta kai ziyara kan kabarin wani babban abokin adawan mahaifin na ta, inda ta yi alƙawarin ɗinke ɓarakar da aka samu tsakanin ɓangarorin biyu na tsawon shekaru 50.

©Kyodo/MAXPPP - 14/09/2012 ; NAHA, Japan - Photo from a Kyodo News aircraft shows the Chinese marine surveillance ship Haijian 51 (front) in Japanese territorial waters near the Japan-controlled Senkaku Islands in the East China Sea on Sept. 14, 2012. China also claims the islets and calls them the Diaoyu Islands. At back is a patrol ship of the Japan Coast Guard. (Kyodo)
Jiragen ruwan China da Japan a gaɓar zibiren da suke taƙaddamaHoto: picture alliance/dpa

A dai-dai lokacin da batun maƙobciyasu Koriya ta arewa da ma batutwan da suka shafi yankin gabashin Asiya suka kasance na gaba a hulɗar ta na harkokin waje, amma abu na farko da shugaba Park za ta sa a gaba shine matsalolin cikin gida, inda yanzu haka taɓarɓarewar tattalin arzikin duniya ya shafi fitar da haja ƙasashen waje. Koriya ta kudu tattalin arzikin ta ya fara tafiyar hawainiya, kana ana ƙara damuwa bisa kuɗin shiga aljihun gwamnati, ga kuma ƙalubalen rashin aikin yi wanda ƙasar ke fama da shi.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu