1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Maraba da korar jagoran sojojin duniya a Afirka ta Tsakiya

Mohammad Nasiru AwalAugust 13, 2015

Kungiyoyin farar hula a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sun nuna farin cikinsu game da murabus din Janar Babacar Gaye shugaban tawagar Majalisar Dinkin Duniya a kasar.

https://p.dw.com/p/1GFIv
General Babacar Gaye
Hoto: picture-alliance/dpa

Wasu kungiyoyin farar hula a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sun yi maraba da murabus din da shugaban tawagar wanzar da zaman lafiya na Majsalisar Dinkin Duniya a kasar Babacar Gaye ya yi bisa zarge-zargen aikata ta'asa da ake wa sojojin Majalisar.

Crepin Mboli-Goumba na wata kungiyar fafutukar kawo sauyi mai ma'ana a Afirka ya ce mutane sun kadu matuka dangane da rahotannin da ke kara bayyana na zargin da ake wa sojojin kiyaye zaman lafiyar na yin lalata da kanana yara.

Shi ma Gervais Lakosso na kawancen kungiyoyin fara hula fata ya yi cewa wannan murabus din zai bude kofar samar da sabon yanayin yarda da juna.

A ranar Laraba babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki Moon ya sanar cewa shugaban rundunar zaman lafiyar ya amsa kiran da aka yi masa kuma ya mika takardar yin murabus.