Kamaru: Garkuwa da mutane 30
January 16, 2019Talla
Wata majiya ta kusa da gwamnati ta bayyana cewa mutanen an yi garkuwa da su ne a kan hanyarsu, tsakanin Buea da Kumba da ke yankin Kudu maso Yammaci. Haka kuma wata kungiya mai zaman kanta ta tabbatar da labarin. Tun dai daga watan Oktoba na shekarar 2017 zaman lafiya a yankin mai magana da harshen Turancin Ingilishi da ke Kudu maso Yamma da makwaftansu na Arewa maso Yamma ke neman ya gagara sakamakon arangama tsakanin 'yan aware da jami'an tsaro, baya ga yawan yin garkuwa da mutane.