1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana sa ran tattaunar za ta daidaita al'amura a Burundi

Abdourahamane HassaneJune 23, 2015

Majalisar Ɗinkin Duniya na shiga tsakanin a rikicin siyasar da ake yi a ƙasar.

https://p.dw.com/p/1FmQp
nach Putschversuch - Präsident Pierre Nkurunziza zurück im Amt
Hoto: Reuters/G. Tomasevic

Manzon musammun na Majalisar ta Ɗinkin Duniya a yankin Afirka ka Tsakiya Abdoulaye Bathily ya jagoranci wata tattaunwa,tsakanin 'yan siyasar haɗe da wakilai na ƙungiyoyin fara hula da na addinai,sai dai wakilan jam'iyyar da ke yin mulki ba su hallarci ganawar ba,

Nan gaba ne a ƙarshen wannan wata za a yi zaɓen 'yan majalisun dokoki da na ƙananan hukumomin a Burundi,wanda ke ciki da rikici kafin zaɓen shugaban ƙasar wanda shugaba Pierre Nkurunziza ya dage ga yin takara ta uku duk kuwa da ƙin amincewar 'yan adawar