An kawo wani da ya kamu da cutar Ebola Jamus
August 27, 2014An kwantar da wani ma'aikacin hukumar lafiya ta duniya WHO da ya harbu da kwayoyin cutar Ebola a asibitin jami'ar birnin Hamburg da ke arewacin Jamus. Kakakin hukumomin kiwon lafiya a Hamburg ya ce hukumar ta WHO ce ta bukaci da a kwantar da ma'aikacin nata a wannan asibiti, da ke zama daya daga cikin asibitocin kararru a Jamus, wanda kuma ke da cikakken tanadi kuma ya san yadda zai tinkari cutar mai saurin yaduwa. Wannan shi ne karon farko da za a yi wa wani da ya kamu da cutar Ebola jinya a Jamus. Alkalumman hukumar WHO sun nuna cewa ya zuwa yanzu ma'aikatan kiwon lafiya fiye da 240 suka harbu da kwayoyin cutar a kasashen Saliyo, Guinea, Liberiya da kuma Najeriya. Sannan 120 daga cikinsu sun rigamu gidan gaskiya.
Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu