An kashe wasu jami'an tsaro na Nijar
October 30, 2014Talla
A cikin wata sanarwa ta haɗin gwiwa wadda ofisoshin ministocin tsaro na Mali da Nijar ɗin suka bayyana, sun ce wasu mayaƙan 'yan ta'adda da ke ɗauke da makamai sun kai wani rukuni na hare-hare a jere.
Wanda a ciki 'yan sanda biyar, da jandarma biyu suka mutu yayin da wasu ukku suka jikkata. 'Yan bindigar sun kai harin ne a kan wani sansanin 'yan gudun hijira na Mali na Mangaize da kuma gidan kurkuku na garin Walam.