1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe wani mallami a Kenya

Abdourahamane HassaneNovember 5, 2014

Hukumomin tsaro na ƙasar sun ce wasu 'yan bindigar waɗanda ba shaidasu ba sune suka harbe mallamin har lahira a birnin Mombasa.

https://p.dw.com/p/1DhCh
Nairobi nach dem Anschlag in Somalier-Viertel
Hoto: Reuters

Mallamin mai sunan Salim Bakari Muwarangi an harbeshi ne da bindiga a sa'ilin da ya fice daga wani masallaci da ke a kudancin ƙasar. Babban sefeto janar na 'yan sanda na Mombasa birnin na biyu mafi girma na ƙasar.

Ya ce mutane da suka harɓe mallamin sun zo ne kan babura kafin daga bisani su ware,kuma ya ce yanzu haka suna gudanar da bincike domin ganosu.A karo da dama ana kashe mallamai masu nuna adawa da Ƙungiyar al Shaabab a ƙasar ta Kenya