An kashe mutane shida a jihar Filato
May 8, 2014Talla
Jami'an tsaro a jihar Filato na ƙoƙarin shawo kan tashin hankalin na ƙabilanci da ya ɓarke tsakanin ƙabilun Irigwe da Rukuba, cikin ƙaramar hukumar Bassa, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 6.
Ko da shi ke dai har ya zuwa wannan lokaci babu wani ƙarin bayyani dangane da sanadin tashin hankalin, to amma rahotannin sun ce an yi harbe-harbe a ƙauyen Dutsen Kura, tsakanin matasa 'yan ƙabilar Irigwe da Rukuba, inda mutane da dama daga ɓangarorin biyu suka sami raunuka. Wasu rahotannin sun ce an yi ƙone-ƙonen gidajen zama na jama'a, lamarin da ya sa wasu mazauna ƙauyen Kaltumai, da Dutsen Kura, suka ƙauracewa tashin hankalin zuwa neman mafaka a wasu ƙauyuka.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu